Bayan APC ta Amince da Shugabancin Abdullahi Abbas, Ganduje yace zasu Sulhunta da su Mal. Shekarau

Date:

Daga Nura Abubakar Bichi

Gwamnan Jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya tabbatar da Cewa uwar jam’iyyar APC ta Kasa ta Amince da Shugabanci Abdullahi Abbas a Matsayin halastacce Shugaban jam’iyyar APC na Jihar kano.
Kadaura24 ta rawaito Gwamnan ya bayyana hakan ne Yayin taron Majalisar Zartarwar ta Jihar Wanda ake yi mako-mako a Gidan gwamnati.
Ganduje yace bayan Mika Rahoto da Sakamakon zaben da aka yi na Shugabanin jam’iyyar APC a kano , jam’iyyar tace batasan kowa a Matsayin Shugaban APCn ba sai Abdullahi Abbas da Sauran Shugabanin da aka zaba.
” Uwar Jam’iyyar APC ta tabbatar Mana da Amince da Shugabanin da muka zaba, ta Kuma ce bata san kowa a Matsayin Shugaban ba sai Waɗanda Muka zaba ” inji Ganduje
Gwamna Ganduje ya Kuma bayyana Cewa yanu suna ta kokarin ganin an sasanta da bangaren su Malam Ibrahim Shekarau, Inda yace dama haka Siyasa ta gada a bata Kuma a zo a Shirya.
Idan ba’a mantaba Kadaura24 ta rawaito Cewa an Sami Rashin jituwa tsakanin bangaren Gwamnati da Kuma bangaren su Malam Ibrahim Shekarau Waɗanda Suke ganin ba’a damawa da su a sha’anin da ya Shafi Shugabancin jam’iyyar APC a kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...