Bayan APC ta Amince da Shugabancin Abdullahi Abbas, Ganduje yace zasu Sulhunta da su Mal. Shekarau

Date:

Daga Nura Abubakar Bichi

Gwamnan Jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya tabbatar da Cewa uwar jam’iyyar APC ta Kasa ta Amince da Shugabanci Abdullahi Abbas a Matsayin halastacce Shugaban jam’iyyar APC na Jihar kano.
Kadaura24 ta rawaito Gwamnan ya bayyana hakan ne Yayin taron Majalisar Zartarwar ta Jihar Wanda ake yi mako-mako a Gidan gwamnati.
Ganduje yace bayan Mika Rahoto da Sakamakon zaben da aka yi na Shugabanin jam’iyyar APC a kano , jam’iyyar tace batasan kowa a Matsayin Shugaban APCn ba sai Abdullahi Abbas da Sauran Shugabanin da aka zaba.
” Uwar Jam’iyyar APC ta tabbatar Mana da Amince da Shugabanin da muka zaba, ta Kuma ce bata san kowa a Matsayin Shugaban ba sai Waɗanda Muka zaba ” inji Ganduje
Gwamna Ganduje ya Kuma bayyana Cewa yanu suna ta kokarin ganin an sasanta da bangaren su Malam Ibrahim Shekarau, Inda yace dama haka Siyasa ta gada a bata Kuma a zo a Shirya.
Idan ba’a mantaba Kadaura24 ta rawaito Cewa an Sami Rashin jituwa tsakanin bangaren Gwamnati da Kuma bangaren su Malam Ibrahim Shekarau Waɗanda Suke ganin ba’a damawa da su a sha’anin da ya Shafi Shugabancin jam’iyyar APC a kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...