Sakon taya Murnar Zama Farfesa Daga Kungiyar Inuwa Kofar mata

Date:

Daga Khadija Abdullahi

Kungiyar bunkasa cigaban unguwar Kofar mata da kewaye mai taken (Inuwar unguwar Kofar mata) ta mika sakon taya murna ga Dr Bala Ado Kofar mata bisa daga darajarsa zuwa matakin Farfesa abangaren ilmin kanana da matsa kaitan sana’o’in dogaro dakai wato
(Professor of Entrepreneurial Studies ) da hukumar gudanarwar jamiar Bayero ta gudanar a makon jiya.

Kazalika kungiyar ta sake mika sakon taya murna ga
Dr. Lubabatu Bello Dan kadai bisa kaiwa ga matakin share faggen zama Farfesa a bangaran ilmin dokokin shari’un kasa masu zaman kansu dana kasuwanci wato (Associate Professor on private and commercial law) a jamiar Bayero dake nan Kano.

Bayanin hakan yana kunshe cikin sanarwar da sakataran yada labaran kungiyar Mal Usman Abdu Kofar mata ya fitar a madadin shugaban kugiyar Mal. Adamu Mararraba da sakataran kungiyar Alhaji Ado Musa Kofar mata (Adori).

Professor Bala Ado wanda dadadden malamine daya jima yana bada gudunmawa a bangaren habaka kananan sana’o’in dogaro dakai sashin ilmin bunkasa kananan sanaoi n jamiar Bayero dake nan yayinda Professor Lubabatu Bello Dankadai itama ta samu yabo a bangaren tallafawa matasa abangaren ilmi a jamiar ta Bayero.

Daga karshe kungiyar ta Inuwar Unguwar Kofar mata ta sake karfafar sabbin Farfesa biyu dasu kara azama akan kokarin da akasansu na ciyar da kasa Nigeria gaba abangaren ilmin da Allah ya fuwace musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...