Rashin Hanya yasa al’ummar Wani Gari kin Yarda a yiwa ‘ya’yansu Allurar Polio

Date:

Daga Rabi’u Usman

Wasu Mutane daga Cikin Al’ummar yankin Garin Unguwar Duniya dake Cikin Karamar Hukumar Dawakin Kudu Sunki Amincewa ayi wa yaran Su Allurar Riga Kafin Cutar Shan Inna Wadda ake Kira da Polio a takaice.

Inda Suka ce Sunfi Bukatar ayi musu aikin Hanya da Kuma Dakatar da Zaizayar kasar da ta Soma Cinye Musu Gidaje da Gonaki a Sakamakon Allurar Polio.

Suna Mai Cewar, Sun Mika Koken Su ga Mahukunta Akan Su Kawo Musu Dauki na Gaggawa Kafin a fara Rasa Rayuka a Cikin Wannan Gari Amma Abin yace tura Kamar yanda Al’ummar ke Shaidawa Wakilin Kadaura24.

Saidai Sakataren Kungiyar Cigaban Matasan garin Unguwar Duniya (Unguwar Duniya youth Development) Auwal Abdulmumini ya Shaida Mana Cewar, Lallai Sun yarda da Riga Kafin, Amma Babbar Bukatar su Shi ne Wannan Hanyar nan, Amma har yanzu Babu Wani Mai rke da Madafun iko da ya Waiwayi Hanyar,Shi isa Suka ce “Zamu Mika Sakon Mu inda Baza Mu iya zuwa ba”

A Nasa Bangaren Dagacin Garin Unguwar Duniya Alhaji Yunusa Lawan ya Bayyana Cewar, Shi da Masu Unguwannin Suna kan Wayar da Kan Mutanen Garin Akan Gudanar da Allurar Riga Kafin Cutar Shan Inna a Garin.

A Karshe dai Sakataren Mulki na Karamar Hukumar Dawakin Kudu Abba Muhammad Inuwa ya Hakur kurtar da Jama’ar garin, Sannan ya Alkawarta Musu Cewar, Karamar Hukumar Nayin Kokarin ganin anyi Musu Wani Abu Mai Muhimmanci akan Matsalar Wannan Hanyar.

A Karshe dai har Wakilin mu ya Baro garin har zuwa Karfe 2pm Ba’a Samu an yiwa Mutanen Garin Polio ba.

Abin jira a gani a Nan Shi ne, Ko Mahukunta Za Suyi Kokari Akan Wannan Gagarumar Matsala a garin Unguwar Duniya?

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...