Buhari Zai tafi Kasar Amuruka

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai tafi kasar Amurka ranar Lahadi domin halartar babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York.

Sanarwar da fadar shugaban ta fitar ta ce a ranar Talata 14 ga watan Satumba za a buɗe taron karo na 76 wanda zai mayar da hankali kan farfadowa daga annobar korona da sake gini mai ɗorewa da girmama haƙƙin ɗan Adam da kuma yadda za a raya Majalisar Ɗinkin Duniya.

A ranar Juma’a shugaba Buhari zai gabatar da jawabi a zauren majalisar, sannan zai keɓe da wasu shugabannin ƙasashe da na hukumomin ci gaban ƙasashen duniya.

Daga cikin tawagar shugaban da za su yi masa rakiya akwai ministan harakokin waje Geoffrey Onyeama da ministan shari’a Abubakar Malami da kuma karamin ministan muhalli Sharon Ikeazor.

Sanarwar ta ce sai a ranar Lahadi 26 ga watan Satumba ake sa ran shugaban zai dawo Najeriya

17 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...