Buhari Zai tafi Kasar Amuruka

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai tafi kasar Amurka ranar Lahadi domin halartar babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York.

Sanarwar da fadar shugaban ta fitar ta ce a ranar Talata 14 ga watan Satumba za a buɗe taron karo na 76 wanda zai mayar da hankali kan farfadowa daga annobar korona da sake gini mai ɗorewa da girmama haƙƙin ɗan Adam da kuma yadda za a raya Majalisar Ɗinkin Duniya.

A ranar Juma’a shugaba Buhari zai gabatar da jawabi a zauren majalisar, sannan zai keɓe da wasu shugabannin ƙasashe da na hukumomin ci gaban ƙasashen duniya.

Daga cikin tawagar shugaban da za su yi masa rakiya akwai ministan harakokin waje Geoffrey Onyeama da ministan shari’a Abubakar Malami da kuma karamin ministan muhalli Sharon Ikeazor.

Sanarwar ta ce sai a ranar Lahadi 26 ga watan Satumba ake sa ran shugaban zai dawo Najeriya

17 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...