Da dumi-dumi: Gwamnatin Tinubu ta bayyana matsayarta kan rikicin siyasar Rivers

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Ministan yaɗa labarai a Najeriya, Idris Malagi ya ce gwamnatin tarayya ba ta da hannu a rikicin siyasar da ake yi a jihar Rivers.

Ministan ya yi magana ne a gidan Talabijin na Channels yau Alhamis inda ya ce kasancewar wasu da ke cikin rikicin na cikin majalisar ministocin Shugaba Bola Tinubu, hakan ba wai yana nufin gwamnatin APC ce ta kitsa halin da ake ciki ba a jihar.

Talla

“Ban gano wata shaida da zan iya cewa gwamnatin tarayya ce take ingiza rikici a jihar Rivers ba,” in ji ministan.

Mun kashe sama da Naira Miliyan 160 Wajen gyara makarantar G.G.C Dala – Shugabar kungiyar DOGAA

Ya ƙara da cewa abu ne mai sauki a yaɗa jita-jita saboda wasu da ke cikin rikicin mutane ne da suke da kusanci da gwamnati”.

Malagi ya bayyana cewa akwai rikicin siyasa a wasu jihohin kamar Ondo kuma Shugaban ya sa baki aka warware rikicin da ya shafi ƴan jam’iyya daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...