Da dumi-dumi: Gwamnatin Tinubu ta bayyana matsayarta kan rikicin siyasar Rivers

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Ministan yaɗa labarai a Najeriya, Idris Malagi ya ce gwamnatin tarayya ba ta da hannu a rikicin siyasar da ake yi a jihar Rivers.

Ministan ya yi magana ne a gidan Talabijin na Channels yau Alhamis inda ya ce kasancewar wasu da ke cikin rikicin na cikin majalisar ministocin Shugaba Bola Tinubu, hakan ba wai yana nufin gwamnatin APC ce ta kitsa halin da ake ciki ba a jihar.

Talla

“Ban gano wata shaida da zan iya cewa gwamnatin tarayya ce take ingiza rikici a jihar Rivers ba,” in ji ministan.

Mun kashe sama da Naira Miliyan 160 Wajen gyara makarantar G.G.C Dala – Shugabar kungiyar DOGAA

Ya ƙara da cewa abu ne mai sauki a yaɗa jita-jita saboda wasu da ke cikin rikicin mutane ne da suke da kusanci da gwamnati”.

Malagi ya bayyana cewa akwai rikicin siyasa a wasu jihohin kamar Ondo kuma Shugaban ya sa baki aka warware rikicin da ya shafi ƴan jam’iyya daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...