Sojojin Nijar sun yanke Wutar Lantarki da Ruwa ga Ofishin Jakadancin Faransa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Shugabannin mulkin soji na kasar Nijar sun yanke wutar lantarki da ruwan sha a ofishin jakadancin kasar Faransa da ke Yamai babban birnin kasar, tare da hana kai musu kayan abinci, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na anadole ya rawaito.

 

Rahotanni sun ce gwamnatin mulkin soji ta kuma dauki irin wannan mataki a karamin ofishin jakadancin Faransa da ke Zinder, Tera, Oualam, Ayorou, Dosso, Yamai, Filingue da sauran wurare.

Talla

Shugaban kwamitin tallafawa na kasa na CNSP Elh Issa Hassoumi Boureima ya bukaci dukkan abokan huldar ofisoshin Faransa da ke Nijar da su dakatar da duk wani aikin samar musu da mai, ruwa, wutar lantarki da kayayyakin abinci.

 

“Muna rokon Nigelec da SPEN (SEEN)) da su katse ruwa da wutar lantarki a ofishin jakadancin Faransa, a cikin karamin ofishin jakadancin Faransa na Zinder da Yamai,” in ji shi.

Ɗan majalisar tarayya na Wudil da Garko ya ƙaddamar da bada tallafi ga kimanin mutane ɗari Uku

Bugu da kari, duk abokan huldar da suka ci gaba da taimakawa Faransawa wajen samar da kayayyaki da ayyuka, za a dauke su a matsayin makiyan al’umma Nijar.

Nijar ta fada cikin rudani ne a ranar 26 ga watan Yuli bayan Janar Abdourahamane Tchiani wanda tsohon kwamandan tsaron fadar shugaban kasar ne ya jagoranci juyin mulkin sojoji da suka hambarar da shugaba Mohamed Bazoum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...