Da dumi-dumi: Tinubu ya Sauyawa Wasu Ministoci Ma’aikatu

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Shugaba Bola Tinubu ya nada Engr. Abubakar Momoh a matsayin Ministan ma’aikatar raya yankin Neja Delta.

Shugaban kasar ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar a daren Lahadi.

Talla

Ma”aikatar raya yankin Neja Delta ta bace a cikin jerin ma’aikatun da aka tura ministoci a makon jiya, lamarin da ya janyo cece-kuce.

Shugaban Mulkin Soji na Nijar ya bayyana lokacin da zasu mika Mulki ga farar hula

A ranar Asabar, kungiyar Pan Niger Delta Forum, PANDEF, ta sha alwashin yin watsi da duk wani yunkurin soke ma’aikatar Neja Delta.

Baya ga shigar yankin Neja Delta, shugaban ya kuma canzawa wasu ministocin ma’aikatu.

Adegboyega Oyetola, wanda da farko aka nada shi Ministan Sufuri, an mayar da shi Ma’aikatar albarkatun kasa, yayin da Bunmi Tunji-Ojo aka mayar da shi a matsayin Ministan Harkokin Cikin Gida.

Jaruma Aisha Humairah ta baiwa masoyanta masu son zuwa wajenta Shawara

Hon. Sa’idu Alkali ya zama Ministan Sufuri.

“Bugu da ƙari, Ministocin biyu a fannin Man Fetur da Gas yanzu suna zaune a Ma’aikatar Albarkatun Man Fetur ta Tarayya tare da sunayen kamar haka:

“(i) Sen. Heineken Lokpobiri shi ne Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur

(ii) Hon. Ekperipe Ekpo shine Hon. Karamin Ministan Gas da Albarkatun Man Fetur.”

Shugaban ya kuma amince da sauya sunan ma’aikatar muhalli da kula da zaizayar kasa ta tarayya zuwa ma’aikatar muhalli ta tarayya.

Sanarwar ta kara da cewa “Duk sauye-sauyen da aka ambata sun fara aiki ne nan take bisa umarnin shugaban kasa.”

A ranar Litinin ne dai za a rantsar da ministocin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...