Shugaban Mulkin Soji na Nijar ya bayyana lokacin da zasu mika Mulki ga farar hula

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Shugaban mulkin soji a Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani ya ce gwamnatinsu da ta hamɓarar da shugaba Mohammed Bazoum, ba za ta wuce shekara uku a kan mulki ba.

Janar ɗin ya bayyana haka ne a jawabinsa ga ‘yan Nijar a kafar talabijin ranar Asabar da yamma.

Talla

Shugaban mulkin sojin kuma ya koka da takunkuman da ƙungiyar Ecowas ta ƙaƙaba wa ƙasar, yana cewa ta yaya za a hana shigar da magunguna cikin ƙasa a bar mutane na mutuwa a asibitoci?

Abin da Bazoum Ya Fada Mana – Shugaban Tawagar ECOWAS, Abdulsalami

“Ba za a tilasta mu amincewa da abin da ba mu yarda da shi ba,” in ji Tchiani.

Ya ƙara da cewa “waɗannan takunkumai sun saɓa wa aƙida da manufar kafa ƙungiyar ta Ecowas ko CEDEAO na yancin kai-komon jama’a da dukiyoyinsu”.

Muna goyon bayan ECOWAS ta dawo da Mulkin Dimokaradiyya Nijar – yan Nijar mazauna Kano

Shugaban sojin ya ce yana tunanin ƙungiyar Ecowas, ba ta auna illar da harin soji zai haddasa a yankin ba.

Tchiani ya ce ƙungiyar ta manta cewa jajircewar sojojin Nijar ce ta hana yankin Afirka ta Yamma aukawa cikin yanayin rashin tabbas

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...