Da dumi-dumi: Tinubu yana ganawa da gwamnonin Nigeria

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban kasar Nigeria Bola Tinubu na ganawa da gwamnonin jihohin kasar 36 a fadar gwamnatin tarayya da ke Abuja.

 

Wannan ce ganawar shugaban ta farko da ƙungiyar gwamnonin ƙasar ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq tun bayan hawansa karagar mulki a makon da ya gabata.

Janye tallafin mai: Gwamnonin jihohi na rage kwanakin aiki

To amma a ranar Juma’ar da ta gabata shugaban ƙasar ya gana da wasu gwamnoni a ƙarƙashin ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki

 

Daga cikin masu halartar ganawar akwai mataimakin shugaban ƙasar Sanata Kashim Shettima da sakataren gwamnatin tarayya Sanata George Akume, da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya, da sauran jami’ai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...