Hukumar Kwastam ta Magantu kan sake bude bodojin Najeriya

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A ranar Talata ne shugaban hukumar hana fasa kwauri ta kasa (NCS) reshen jihar Ogun 1, Bamidele Makinde, ya tabbatar da sake bude iyakar Idiroko a jihar Ogun.

 

Makinde ya ce an sake bude iyakar tun shekarar da ta gabata, sabanin wani faifan bidiyo da ya nuna yadda wasu mazauna Idiroko ke murnar sake bude iyakar.

 

A watan Agustan 2019 ne tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rufe dukkan iyakokin kasa a wani bangare na kokarin dakile fasa kwauri da bunkasa noman shinkafa a cikin gida.

Janye tallafin mai: Gwamnonin jihohi na rage kwanakin aiki

A shekarar 2020, Buhari ya bayar da umarnin bude iyakokin a Seme a Legas, Illela a Sokoto, Maigatari a Jigawa, da Mfum a Cross River.

 

Kuma a cikin watan Afrilu, 2022, Buhari ya kuma ba da umarnin sake bude wasu kan iyakokin hudu da suka hada da Idiroko a Ogun, Jibiya a Katsina, Kamba a Kebbi da Ikom a Cross River.

Sai dai wani faifan bidiyo na dakika 21 da ke nuna yadda wasu jami’an hukumar kwastam ke gudanar da aikin sake bude kan iyakar Idiroko cikin farin ciki a ranar Litinin.

Da yake mayar da martani yayin ganawa da manema labarai a Abeokuta, Makinde ya ce tun wancan lokacin ne aka bude kan iyakar Idiroko sabanin yadda hoton bidiyo ya nuna.

Ya ce an bude iyakar Idiroko tare da Jibiya a Katsina, Kamba a Kebbi da kuma Ikom a Cross River.

Makinde, ya ce sauran iyakokin kasa a jihar kamar Imeko, Ohumbe, Ijofin da Ijoun na nan a rufe.

Ya ce, “A jihar Ogun, kamar yadda muke magana a yau muna da iyakokin da aka amince da su sama da shida, Imeko, Ijofin, Ijoun, Ohunbe, muna da shida daga cikinsu. Idiroko ne kawai aka bude yanzu, sauran suna nan a kulle.

“Yanzu, mun sami sabuwar gwamnati kuma mu ma’aikatan gwamnati ne kawai, muna aiwatar da manufofi da duk abin da gwamnatin ta ce muna yi.

“Don haka, Idiroko tana nan buɗe 24/7, amma sauran, ba mu da ikon buɗe su. Idan ku ka shigo da kayan kasuwanci ta can dole zamu, za mu kwace kayanku.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...