Daga Rukayya Abdullahi Maida
Yayin da ya rage Kwanaki biyar wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kare, ministoci sun fara kokarin mika ragamar ma’aikatunsu ga manyan sakatarorin su gabanin rushe majalisar ministocin, inji rahoton Daily Trust.
A ranar litinin 29 ga watan Mayu 2023 wa’adin mulkin shugaba Buhari na shekaru 8, zai kare wanda ya fara daga ranar 29 ga watan Mayun 2015.
An fara gudanar da shirye-shiryen rantsar da zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, a mako mai zuwa , Inda za a gudanar da taron bikin rantsuwar a dandalin Eagle Square da ke Abuja da misalin karfe 10 na safe ranar.
Da dumi-dumi: Ganduje ya rushe majalisar zartarwarsa
Ana sa ran a yau Laraba Ministan tsaro Bashi magashi zai ajiye aikin sa gabanin Shugaban kasa Muhammad Buhari ya bada umarnin rushe majalisar zartarwarsa.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa tuni janar Bashir Salihi magashi ya baiwa babban Sakataren ma’aikatar Ibrahim Kana da ya cigaba da tafiyar da ragamar ma’aikatar.
Tsohon Firaministan Burtaniya ya ziyarci Tinubu a Abuja
Wani jami’i a ma’aikatar ya ce ministan ya shaida wa Kana cewa tunda aikin gwamnati ci gaba ne, ya kamata ya tafiyar da duk wasu batutuwan da suka shafi kasafin kudi da kwangiloli bisa tsarin dokar ma’aikatar.
Majiyar Kadaura24 ta rawaito a yau ne za a gudanar da wani liyafar cin abinci domin karrama ministan bisa yadda ya gudanar da aiki a ma’aikatar. A wata sanarwa da ya aike wa daya daga cikin wakilan majiyar ta mu, babban sakatare ya ce Magashi ya cancanci karramawa saboda “salon shugabancin sa”.
“Babban Sakataren ma’aikatar tsaron yace an shirya liyafar cin abincin daren ne don karrama Ministan Tsaro, Janar Bashir Salihi Magashi, bisa la’akari da irin kwazonsa da salon shugabancinsa wajen tsarawa da magance kalubalen da ake fuskanta a fannin tsaro a Najeria.