Shafukan sada zumunta na da hadari ga lafiyar matasa – Masana

Date:

Wani babban jami’in lafiya a kasar Amurka ya fitar da gargadi kan hadarin shafukan sada zumunta ga yara da matasa.

Dr Vivbek Murthy, wanda shi ne shugaban ma’aikatar lafiya ta Amurka ya ce kafofin sada zumunta da muhawara da kananan yara da matasa ke amfani da su na haifar da manyan kalubale ga lafiyar jiki da rayuwarsu.

Sannan suna haddasa matsalar rashin cin abinci da jefa masu amfani da su cikin damuwar rashin yarda da kai.

BBC Hausa ta rawaito Rahoton ya ce matakan da ake dauka domin rage damar da yara ke da ita ko matasa a shafukan sada zumunta ba sa aiki.

Sannan kuma akwai sauran jan aiki a binciken gano cikakken tasirin da wadannan shafuka ke yi a rayuwar matasa.

Sai dai kuma duk da wannan gargaɗi masanin ya ce akwai wasu alfanu da waɗannan shafuka kan yi ga wasu rukuni na mutane a rayuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...