Sarkin Kano Aminu Ado Bayero Ya yiwa Alhaji Aminu Dantata Ta’aziyyar Rasuwar Matarsa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi ta’aziyya ga hamshakin dan kasuwar nan kuma dattijon Alhaji Aminu Alhassan Dantata CON da daukacin iyalan Dantata bisa rasuwar matarsa ​​Hajiya Rabi Aminu Alhassan Dantata.

 

Mai Martaba ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa mai tarin dukiya, kuma uwa mai tarbiyya wacce ta tsara rayuwar mutane da dama da ke kusa da ita ta yadda za su kasance masu inganci da adalci.

Goman ƙarshe: Ya kamata matasa ku kashe Datar wayoyin ku, ku daina kallon TV – Dr. Ali Tamasi

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24.

 

Sarkin wanda ya aika da tawaga karkashin Wazirin Kano Alhaji Sa’adu Shehu Gidado yana mika ta’aziyyarsa a madadin mai martaba Sarkin Kano da Majalisar Masarautar Kano da kuma al’ummar Jihar Kano. Ya jajanta wa dattijon mai daraja, uba mai hangen nesa kuma mai fatan alherin samar da ci gaba, Alhaji Aminu Alhassan Dantata bisa rasuwar matarsa.

 

Ƙasar Ingila za ta dakatar da daukar ma’aikatan kiwon lafiya daga Najeriya

Mai Martaba Sarkin, ya bayyana rasuwar Hajiya Rabi Aminu Dantata a matsayin babban rashi ba ga iyalanta da jihar Kano kadai ba, har ma ga sauran al’ummar da kuma Najeriya baki daya.

 

Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan marigayiyar yasa tana cikin Jannatul firdaus tare ya kuma bawa ‘yan uwa da iyalansa hakurin jure rashinta ya kuma ce wannan rashin wani babban rashi ne da ba za’a iya kwatantawa ba.

 

Sauran ‘yan tawagar sun hada da Walin Kano Alhaji Bashir Mahe Bashir da Dan Ruwatan Kano Alhaji Ibrahim Hamza Bayero da kuma sakataren mai martaba Sarki Alhaji Abdullahi Haruna Kwaru.

 

Da yake karbar tawagar a madadin iyalan Dantata, Alhaji Turado Dantata ya mika godiyarsa ga mai martaba Sarkin Kano bisa ziyarar ta’aziyyar da ya kai masa, sannan ya kuma jajantawa sarkin bisa wannan banban rashi da akayi. Ya yi addu’ar Allah ya karawa jihar mu kano da Najeriya lafiya, zaman lafiya da kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...

Hukumar almajirai da yaran da ba sa zuwa Makaranta ta kaddamar da yi wa yaran da ba sa zuwa Makaranta Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...