An haramtawa limamai karanta Qur’ani daga wayar hannu a lokacin Tarawi da Tahajjud

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Ma’aikatar kula da harkokin addinin Musulunci da wakafi ta kasar Kuwait ta bayyana haramta wa limamai karanta Alƙur’ani daga wayoyinsu na hannu a lokutan sallolin nafilfilun dare na watan Ramadana.

 

Jaridar Al-Rai ta ruwaito cewa hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ta samu sa hannun ƙaramin minista mai kula da harkar masallatai, Salah Al Shilahi.

 

Goman ƙarshe: Ya kamata matasa ku kashe Datar wayoyin ku, ku daina kallon TV – Dr. Ali Tamasi

Sanarwar ta ƙarfafa wa limamai gwiwa da su riƙa amfani da haddarsu ta Ƙur’ani a lokutan sallolin Tarawihi da Tahajjud, kasancewar su (limaman) misali ne ga sauran al’umma.

Ƙasar Ingila za ta dakatar da daukar ma’aikatan kiwon lafiya daga Najeriya

Ta ƙara da cewa ya kamata kowane limami ya yi muraji’ar karatunsa yadda ya kamata gabanin jan sallah a maimakon karantowa daga cikin waya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...