Hajjin bana: NAHCON ta baiwa jihar Kano gurbin alhazai Sama da dubu 5

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

 

Hukumar Alhazai ta Ƙasa, NAHCON ta baiwa Jihar Kano gurbin alhazai dubu 5902 domin zuwa aikin Hajjin bana, 2023.

 

Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, Muhammad Abba Dambatta ne ya bayyana hakan a yau Asabar yayin ƙaddamar da shirin bita na wannan shekara a Kano.

 

Talla

Alhaji Danbatta ya ce tuni kimanin maniyyata dubu 4 suka biya kudin ajiya.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Danbatta, ya ce gwamnatin jihar ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da ayyukan Hajjin da ke tafe ba tare da tangarda ba.

 

Ya ce hatta aikin Hajjin bara da aka samu matsaloli, jihar Kano ta taka rawar gani inda wanda ya kai ga samun lambobin yabo da dama musamman daga ƙungiya Hajj Reporters.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...

NNPPn Kano ta bayyana matsayar Kwankwaso kan batun yi wa Tinubu mataimaki a 2027

Shugabanin bangarori biyu na jam’iyyar NNPP a jihar Kano,...

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...