Daga Rahama Umar Kwaru
Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin da ake yadawa cewa George Akume ya ajiye aikinsa na Sakataren gwamnatin tarayya.
Kadaura24 ta rawaito A dare ranar asabar ne dai wasu mutane a shafukan sada zumunta suka rika yada cewa Wai George akume ya yi murabus daga mukaminsa na Sakataren gwamnatin tarayya.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Kasa Bayo Onanuga ya fitar ya ce labarin na shi da tushe ballantana makama.
Ya ce Shugaban Kasa ba ma ya kasar ballantana a yi Maganar ya sauke wani ko ya nada wani inda ya bukaci al’umma da su yi watsi da labarin ba shi da tushe.
Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata
Sanarwar ta ce babu wani sabon sauyin mukami da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, duk da cewa yana halartar taro a ƙasar Saint Lucia.
Ta ce rahoton da ke yawo game da sauya Akume labari ne na ƙarya da masu tayar da hankali suka kirkira.
Fadar Shugaban Ƙasa ta shawarci ’yan Najeriya da su yi watsi da labaran ƙarya da ake yaɗawa, tana mai jaddada cewa George Akume na ci gaba da kasancewa a matsayin SGF.