A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin da ake yadawa cewa George Akume ya ajiye aikinsa na Sakataren gwamnatin tarayya.

Kadaura24 ta rawaito A dare ranar asabar ne dai wasu mutane a shafukan sada zumunta suka rika yada cewa Wai George akume ya yi murabus daga mukaminsa na Sakataren gwamnatin tarayya.

InShot 20250309 102512486
Talla

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Kasa Bayo Onanuga ya fitar ya ce labarin na shi da tushe ballantana makama.

Ya ce Shugaban Kasa ba ma ya kasar ballantana a yi Maganar ya sauke wani ko ya nada wani inda ya bukaci al’umma da su yi watsi da labarin ba shi da tushe.

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Sanarwar ta ce babu wani sabon sauyin mukami da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, duk da cewa yana halartar taro a ƙasar Saint Lucia.

Ta ce rahoton da ke yawo game da sauya Akume labari ne na ƙarya da masu tayar da hankali suka kirkira.

Fadar Shugaban Ƙasa ta shawarci ’yan Najeriya da su yi watsi da labaran ƙarya da ake yaɗawa, tana mai jaddada cewa George Akume na ci gaba da kasancewa a matsayin SGF.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...