Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhinin sa kan rasuwar dattijo, fitaccen ɗan kasuwa kuma mai bayar da gudunmawar al’umma, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, wanda ya rasu yana da shekaru 94 a safiyar Asabar, 28 ga Yuni, 2025.

A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana marigayi Dantata a matsayin jarumin ƙasa da kuma babban rashi ga Najeriya, sakamakon gagarumar gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban tattalin arzikin ƙasar.

InShot 20250309 102512486
Talla

“Alhaji Dantata zai ci gaba da kasancewa cikin tarihin Najeriya saboda kwazonsa, jajircewarsa, da kishin ƙasa da ya nuna ta hanyar sana’o’in kasuwanci da ayyukan jin ƙai da suka shafi rayuwar dimbin ‘yan Najeriya,” in ji Shugaba Tinubu.

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Marigayin ya shahara da basirarsa a harkar kasuwanci, kuma ya taka rawar gani a fagen hidimar jama’a, inda ya taba zama Kwamishinan Tsare-tsare da Ci Gaban Tattalin Arziki a tsohuwar Jihar Kano da sauran muhimman mukaman gwamnati.

Shugaba Tinubu ya kuma ambato irin alaƙar da ke tsakaninsa da marigayin, inda ya bayyana shawarwarin da ya ba shi da goyon bayan da ya nuna masa a matsayin abin karfafa gwiwa da amfani ƙwarai.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Haka kuma, shugaban ya yaba da ayyukan jin ƙai na Alhaji Dantata, musamman a fannonin ilimi da kula da lafiya, wadanda suka taimaka wa rayuwar mutane da dama a fadin ƙasa.

Shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, Gwamnatin Kano da al’ummar jihar bisa wannan babban rashi, yana mai cewa Najeriya ta rasa ɗaya daga cikin fitattun ‘ya’yanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...