Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana alhinin sa bisa rasuwar dattijo, fitaccen ɗan kasuwa kuma mai bayar da gudunmawar al’umma, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, wanda ya rasu yana da shekaru 94 a safiyar Asabar, 28 ga Yuni, 2025.
A wata sanarwa da Gawuna ya sanyawa hannu da hannunsa wacce kuma aka aikowa Kadaura24, ya bayyana marigayi Dantata a matsayin wanda ya ba da gudunmawa sosai wajen ci gaban tattalin arzikin ƙasar.

“Alhaji Dantata zai ci gaba da kasancewa cikin tarihin Najeriya saboda kwazonsa, jajircewarsa, da kishin ƙasa da ya nuna ta hanyar gudanar da kasuwanci da ayyukan jin ƙai da suka taba rayuwar dimbin ‘yan Najeriya,” in ji Gawuna

Gawuna wanda shi ne ya yi wa jam’iyyar APC takarar gwamna a zaben da ya gabata ya cewa “Marigayin ya shahara a harkar kasuwanci, kuma ya taka rawar gani a fagen hidimtawa jama’a, inda ya taba zama Kwamishinan Tsare-tsare da Ci Gaban Tattalin Arziki a tsohuwar Jihar Kano da sauran muhimman mukaman gwamnati.
Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata
Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, Gwamnatin Kano da al’ummar jihar bisa wannan babban rashi, yana mai cewa Najeriya ta rasa ɗaya daga cikin fitattun ‘ya’yanta.