NiMet ta bayyana jihohin da za a sami tsawa da ruwan sama na kwanaki 3 a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta yi hasashen za a iya samun tsawa da ruwan sama a sassan Najeriya daban-daban daga ranar Lahadi 8 ga watan Yuni zuwa Talata 11 ga watan Yunin 2025.

Hukumar hasashen yanayin ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar a Abuja.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Inda ta ce za a iya samun wannan yanayin a a sassa da dama na kasar, da suka hada da jihohin Arewa maso yamma, Arewa ta Tsakiya, da Kudancin kasar.

A cewar NiMet, ana sa ran ranar Lahadi za a fara da ganin gajimare a wurare da dama, amma zuwa yammacin ranar yanayi zai canza .

Sarki Sanusi ya hori musulmi su hada kai don cigaban addinin musulunci

Hukumar ta bayyana cewa “da rana ko yamma, ana iya samun tsawa tare da ruwan sama a sassan Taraba, Adamawa, Katsina, Kano, Zamfara, Kaduna, Jigawa, Borno, Gombe, da Bauchi.”

InShot 20250309 102403344

“A shiyyar Arewa ta Tsakiya, da safe ana sa ran za a sami gajimare a yankin.

“Washegari kuma ana hasashen tsawa da ruwan sama a wasu sassan babban birnin tarayya, Neja, Nasarawa, Kwara, Kogi, Benue da Plateau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...