Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Mai rikon mukamin shugaban kungiyar yan Jarida ta Kasa reshen jihar Kano Mustapha Gambo Muhammad ya rantsar da Sabon shugaban kungiyar reshen gidan Radio Nigeria Pyramid Fm Kano.
Da yake jawabi Mustapha Gambo ya bukaci Sabon shugaban da ya Maida hankali wajen hada kan ya’yan kungiyar domin samar da cigaba mai ma’ana .

“Hadin Kai shi ne kashin bayan cigaban Kowacce al’umma, don haka ina kira a gareka da kai yi iya bakin kokarinka don samar da hadin Kai wanda shi ne zai Kai Wannan kungiya ga sabon cigaba”. Inji Mustapha Gambo Muhd.
Mukaddashin shugaban na NUJ ya kuma yi kira ga ya’yan kungiyar da sauran Shugabannin kungiyar da su baiwa Sabon shugaban hadin kai da goyon baya domin ya Sami nasarar ciyar da kungiyar gaba.
Yansanda sun Haramta Hawan Sallah a Kano
Da yake nasa jawabin sabon shugaban kungiyar yan jarida reshen gidan Radio Nigeria Pyramid Abdullahi Muhammad ya yi alkawarin yin aiki bisa Gaskiya da adalci ba tare da nuna banbanci ba .
” Babu shakka wannan muhimmiyar rana ce a wajena da ita wannan kungiya, kuma Ina ba ku tabbacin na zo da Tsare-tsare da za su ciyar da kungiyar nan ta mu gaba”. Inji Abdullahi Muhammad
Ya ce ya na kira ga daukacin ya’yan kungiyar da su ba shi hadin Kai da goyon baya domin aiwatar da tsare-tsaren da ya zo da su don inganta cigaban kungiyar da Samar da walwala ga ya’yan kungiyar.
Abdullahi Muhammad dai ya maye gurbin Aminu Abba Kwaru ne wanda ya Sami sauyin wurin aiki daga Pyramid Fm zuwa Ma’aikatar Kula da ingantuwar aiyuka ta Kasa.