Za a kashe Naira Miliyan 87 wajen Sanya Interlock a sakatariyar K/H Dala – Surajo Imam

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Gwamnatin jihar Kano ta Amince da kashe Sama da Naira Miliyan 87 dan aiwatar da Aikin Shimfida Interlock a sakatariyar Karamar Hukumar Dala

Shugaban Karamar Hukumar Alhaji Surajo Ibrahim Imam shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da Jami’ar Hulda da Jama’a ta Karamar Hukumar Dala Hassana Aminu ta aikowa Kadaura24.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Shugaban Karamar Hukumar Dala Surajo Imam yan a mai cewar tun Alif 1989 da kafuwar Karamar Hukumar ba ta samu wani sauyi ba sai a wannan lokacin.

Yansanda sun Haramta Hawan Sallah a Kano

Ya kara da cewar hakan ya na daga cikin manufofin gwamnatin Kano na kawo sauyi da Cigaba Mai ma’ana a matakai daban daban

Surajo Imam yace izuwa yanzu tuni an biya Sama da Miliyan 47 na kudin Aikin, Yana Mai cewar baya Ga wannan kuma akwai Wani Shirin na fentin Karamar Hukumar Dalan da sauya kofofi, Hadi da Gina sabuwar majalisar Kansiloli bisa irin hadin kai da suke Bashi dan Ciyar da Karamar Hukumar Gaba.

InShot 20250309 102403344

A Jawabin Sa Shugaban sashin Ayyuka na Karamar Hukumar Dala Alhaji Shafi’u Musa Zakarai ya bayyana da Kaddamar wannan mahimmin Aiki da nufin zamunantar da Karamar Hukumar Dala

Shi ma a nasa bangaren Malam Shafi’u Gwarzo bukaci ma’aikatan karamar hukumar da su kula da kayayyakin aikin da aka samar domin amfanin su yadda ya kamata, dan ciyar da yankin Gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...