Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh, ya ce duk zarge-zargen da ake yi masa, musamman na kin yin aiki da wasu ma’aikata a hukumar, ba gaskiya ba ne.
Farfesa Saleh ya musanta zarge-zargen da wasu ke yi masa, inda ya ce wasu rashin fahimtar ayyukan shugabannin hukumar da ma na hukumar ne ya janyo hakan.

Ya kara da cewa ikirari na ajiye ƴan kwamitin da ba na zartarwa ba na hukumar ba shi da tushe balle makama.
A cewar sa, wadanda ba sa cikin kwamitin zartaswa ba su da wata takamaimiyar rawar da zai su taka a dokance.
Daily Nigerian