Babu wanda ya hana ni shiga Fadar Shugaban Kasa – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa babu wanda ya hana shi shiga fadar Shugaban Kasa ta Aso Rock Bill, inda ya bayyana labarin a matsayin mummunan rahotannin da ake yadawa.

A daren Juma’ar da ta gabata ne rahotanni a shafukan internet su ka bayyana cewa wasu jami’an tsaro sun hana mataimakin shugaban kasar shiga Villa, kuma an tsare shi a gidansa har sai shugaban kasa ya dawo daga tafiyarsa zuwa kasashen waje.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Mista Stanley Nkwocha, babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da sadarwa, ofishin mataimakin shugaban kasar, ya ce labarin ba gaskiya ba ne.

Da dumi-dumi: Kamfanin NNPC ya rage farashin man fetur a Nigeria

A cewarsa, irin wadannan munanan bayanai ba za su iya nishadantar da su ba sai wadanda ba su san ayyukan cikin gida na gwamnatin Najeriya ba.

Ya ce, a ‘yan kwanakin nan, da gangan da kuma tsare-tsare aka yi ta shirya karya a kan ofishin mataimakin shugaban kasa ta fuskoki da dama.

InShot 20250309 102403344

Wannan yunƙuri ne na rashin na cin zarafin mutum da ofishin mai girma mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima.

Nkwocha ya ce a farkon makon nan ne fadar shugaban kasa ta yi watsi da irin wannan labarin na karya dangane da alhakin yada hotunan yakin neman zaben da ke dauke da hotunan shugaba Bola Tinubu.

 

Ya ce Shettima ya ci gaba da mai da hankali kan ayyukan sa da kuma marawa shugaban kasa baya wajen cimma muradun ‘yan Najeriya.

Nkwocha ya yabawa ‘yan Najeriya a kowane bangare da ke ci gaba da nuna fatan alheri ga gwamnatin Tinubu kuma suka dauki nauyin yaki da yada labaran karya.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...