INEC ta karbi takardar neman yi wa Sanata Natasha kiranye

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa ta karɓi ƙorafi da ke neman fara yunƙurin yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kiranye a matsayin Sanata.

Sakataren hukumar, Rose Oriaran-Anthony ce, ta karɓi ƙorafin a yau Litinin.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ƴan mazaɓar, a wata wasika da jagoran su, Salihu Habib ya sanyawa hannu, sun nuna cewa sun dawo daga rakiyar wakilcin Natasha a majalisar dattawa.

Masu korafin, karkashin ƙungiyar Concerned Kogi Youth and Women, sun yi kira ga INEC da ta gaggauta sahale yunƙurin kiranyen, wanda su ka ce hakan hakan na da kyau wajen karfafa dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Hakan ya zo ne bayan da tun a farko, kotu ta hana INEC karɓar korafi na yunkurin yi wa Natasha kiranye, amma kuma wanne tudu wanne gangare, sai kotun a yau Litinin ta baiwa hukumar zaben damar karbar korafe-korafen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hawan Sallah: Yansandan Kano sun gayyaci hadimin Sarki Sanusi II bayan mutuwar wani

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...

Barka da Sallah: Gwamnan Kano ya bukaci yan jihar su rungumi zaman lafiya da adalci

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Sarki Aminu da Sarki Sanusi sun bukaci gwamnati ta hukunta duk masu hannu a kisan Mafarautan Kano a Edo

Daga Aliyu Danbala Gwarzo da Sani Idris maiwaya   Mai Martaba...

Murtala Sule Garo ya yiwa Kanawa Barka da Sallah

Ina taya daukacin al’ummar Musulmi maza da mata musamman...