INEC ta karbi takardar neman yi wa Sanata Natasha kiranye

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa ta karɓi ƙorafi da ke neman fara yunƙurin yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kiranye a matsayin Sanata.

Sakataren hukumar, Rose Oriaran-Anthony ce, ta karɓi ƙorafin a yau Litinin.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ƴan mazaɓar, a wata wasika da jagoran su, Salihu Habib ya sanyawa hannu, sun nuna cewa sun dawo daga rakiyar wakilcin Natasha a majalisar dattawa.

Masu korafin, karkashin ƙungiyar Concerned Kogi Youth and Women, sun yi kira ga INEC da ta gaggauta sahale yunƙurin kiranyen, wanda su ka ce hakan hakan na da kyau wajen karfafa dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Hakan ya zo ne bayan da tun a farko, kotu ta hana INEC karɓar korafi na yunkurin yi wa Natasha kiranye, amma kuma wanne tudu wanne gangare, sai kotun a yau Litinin ta baiwa hukumar zaben damar karbar korafe-korafen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...