Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

Date:

 

 

Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero yayi wata ganawa ta sirri da Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu mintina kadan kafun tashinsa zuwa kasar Faransa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran Sarkin Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Ganawar da Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi da shugaban kasar tana da nasaba ne da iftila’in daya faru ga al’umar Rimin Zakara dake yankin Karamar Hukumar Ungogo a jihar Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyanawa shugaban kasar damuwarsa matuka bisa yadda al’ummar suka shiga damuwa kan yadda aka samu rasa rayuka da dukiyoyi da kuma yadda wasu suka samu jikkata.

Shugaban ya tabbatarwa da Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero cewa za’ayi duk mai yuwuwa domin ganin an warware takaddamar tareda tabbatar musu da matsugunansu.

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Shugaba Tinubu ya nuna alhininsa tareda jajantawa mai martaba sarkin bisa abunda ya samu al’umarsa inda ya yabawa sarkin kan yadda ya damu da damuwar al’umar jihar Kano.

Wannan ziyara dai da mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya kai zuwa wajan shugaban Kasar bata da wata nasaba da tafiyar da Sunusi Lamido yayi zuwa Abuja kamar yadda wasu a kafafan sada zumunta na zamani ke yadawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...