Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Date:

Daga Nazifi Dukawa

 

Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar Hukumar Ungoggo a jihar Kano sun nuna bacin ransu bayan da suka zargi wasu jami’an tsaro tare da rakiyar motocin rushe gurare suka hallarci unguwar inda suka fara rushe gidaje da kwangayen dake yankin.

Hakan dai ya fusata al’ummar yankin har suka kone Gidan mai gari, da suka ce da shi aka hada baki aka cucesu.

Abubakar Mika’ilu mazaunin unguwar ne ta Rimin zakara ya shaidawa kadaura24 cewa suna zargin ma’aikatar Kasa da tsare-tsare ta jihar Kano da jami’ar Bayero da wata runduna ta musamman ta da kunshi jami’an tsaro daban-daban sune suka shiga unguwar tasu cikin dare domin rushe musu gidajensu.

InShot 20250115 195118875
Talla

” Anzo cikin dare za a rushe mana gidaje hakan tasa aka kashe mana yara kusan 3 tare da karbin wasu matasan guda 6 , Muna kira ga gwamnan jihar Kano da ya sa baki akan Wannan lamari domin mu ko za’a karar da mu ba mu bari a zalunce mu ba”. Inji Abubakar Mika’ilu

Guda cikin iyayen yaran da aka kashe, ya ce sun cika da mamakin yadda gwamnati da ya kamata ta kare rayukan al’umma kuma ta buge da kashe mutane.

Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Ya bukaci gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya bincika tare da hukunta duk wanda yake da hannu wajen kashe musu ya’yansu.

Ana dai fargabar jami’an tsaron sun harbi wasu mutane shida, an kuma yi jana’izar mutane biyu.

Kadaura24 ta tuntubi daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar kasa ta Kano,inda ya ce suna gudanar da bincike kan lamarin, da zarar sun gama kwamishinan ma’aikatar zai sanar da mu halin da ake ciki.

Hakama, da muka tuntubi Kakakin Rundunar yan sanda ta Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce suna gudanar da bincike kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Masarautar Gidan Igwai ta dakatar da Usman Umar wanda...