Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Date:

Masarautar Gidan Igwai ta dakatar da Usman Umar wanda akafi saninsa da (SOJA BOY) daga sarautar Yariman Gidan Igwai dake jihar Sokoto da Masarautar ta bashi a baya.

A wata sanarwa da ta fito daga Marafan Sarkin adar, mai dauke da sa hannun Alhaji Abubakar Marafan, Masarautar ta ce ta tube rawanin Sojaboy saboda wasu dalilai da suka bayyana.

InShot 20250115 195118875
Talla

A cewar Sanarwar ‘An samu bidiyon sa yana aikata abubuwan da suka sabawa addini, al’ada da dabi’un mutanen Gidan Igwai. Bisa wannan dalili ne masarautar ta yanke hukuncin dakatarwa tare da tsige shi daga sarautarsa.

Waiya ya kaddamar da kungiyar masu tallata aiyukan gwamnan Kano a Facebook

Hakazalika, Sanarwar ta bayyana irin yadda al’ummar yankin su yi tir da wannan dabi’a kuma sun nesanta kansu daga wannan abu mara kyau. Da tsohon basaraken yake aikatawa a wakokinsa.

Daga karshe masarautar tayi nasiha ga tsohon basaraken akan yaji tsoron Allah ya rungumi dabi’u irin na karantarwar addinin Musulunci.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito hukumar tace fina-fina ta jihar Kano ta ce ta dakatar da Sojaboy saboda wasu bidiyoyi na badala da ya ke yadawa da sunan wakoki ko fina-finan Kannywood.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...