Sarkin Musulmi ya bayar da umarnin fara neman watan sha’aban a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ba da umarnin a fara duban jinjirin watan sha’aban a gobe laraba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci Farfesa Sambo Wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka raba manema labarai a sokoto.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-naden Mukamai

Sarkin Musulmin ya ce duk wanda ya ga watan ya kai rahoton zuwa ga mai unguwarsu ko dagaci domin sanar da fadar Sarkin Musulmin don sanar da ganin watan a hukumance.

Ganin watan na sha’aban dai shi ke nuna cewa watan Ramadan ya karo, domin a kalandar addinin musulunci daga watan sha’aban sai Ramadan Wanda al’ummar Musulmin duniya suke gudanar da ibadar azumi a cikinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...