Gwamnan Kano ya nada mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nada Ibrahim Adam a matsayin mai bashi shawara ta musamman a kan harkokin yada labarai.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ibrahim Adam, matashi ne mai kimanin shekaru 32 ya yi digirinsa a jami’ar Bayero inda ya karanci kimiyar Siyasa (Political Science), yana daga cikin matasan da suke yada manufofin gwamnatin jihar Kano.

Sarkin Musulmi ya bayar da umarnin fara neman watan sha’aban a Nigeria

A baya dai ya zama hadimin Alhaji Abba Kabir Yusuf lokacin yana matsayin dan takarar gwamnan Kano daga shekara ta 2020 zuwa 2022, daga baya kuma ya koma aiki a matsayin PA na Rabiu Musa Kwankwaso.

Gwamnan ya taya Ibrahim Adam murna, sannan ya bukaci ya yi amfani da kwarewarsa wajen cigaban gwamnatin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...