Sarkin Musulmi ya bayar da umarnin fara neman watan sha’aban a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ba da umarnin a fara duban jinjirin watan sha’aban a gobe laraba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci Farfesa Sambo Wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka raba manema labarai a sokoto.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-naden Mukamai

Sarkin Musulmin ya ce duk wanda ya ga watan ya kai rahoton zuwa ga mai unguwarsu ko dagaci domin sanar da fadar Sarkin Musulmin don sanar da ganin watan a hukumance.

Ganin watan na sha’aban dai shi ke nuna cewa watan Ramadan ya karo, domin a kalandar addinin musulunci daga watan sha’aban sai Ramadan Wanda al’ummar Musulmin duniya suke gudanar da ibadar azumi a cikinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...