Dalilin da ya sa yan Najeriya suka kwana cikin duhu ranar Litinin

Date:

 

 

Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarki na ƙasar a ranar Litinin.

Layin ya lalace ne da misalin ƙarfe 7 na yamma, kamar yadda sanarwa daga kamfanin rarraba lantarki ta ƙasa (TCN) ya bayyana.

Talla

Lamarin ya jefa miliyoyin ‘yan ƙasar da kuma sana’o’insu cikin duhu.

Wannan dai shi ne karo na biyar da layin ke lalacewa a shekarar 2024.

Abba tsaya da kafarka: Sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Shi ma kamfanin rarraba hasken wutar lantarki reshen jihar Kano (KEDCO) ya nemi afuwar kwastomominsa kan abin da ya faru a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X.

“Muna bakin cikin sanar da ku cewa an samu ɗaukewar wuta ne sakamakon matsalar da aka samu a layin wuta na ƙasa,” kamar yadda shugaban sashen sadarwa na kamfanin Sani Bala ya bayyana.

Ya ce hakan ne ya janyo rashin rarraba wutar zuwa ga kwastomomi.

“Muna rokon al’umma da su yi hakuri yayin da muke ci gaba da aiki tukuru don shawo kan matsalar ta faru da kuma mayar da wutar lantarki yadda muka saba,” in ji shi.

Talla

Ya buƙaci mutane da su kula sosai wajen kare kai daga masu sata ko lalata wayoyin wutar lantarki.

Mene ne babban layin wutar lantarki na Najeriya kuma yaya yake aiki?

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...