Adadin yaran da ke fama da yunwa ya karu a Arewacin Nigeria – Bincike

Date:

Ƙungiyar agaji ta likitoci Médecins Sans Frontières (MSF) ta ce a cikin watanni takwas ɗin farko na wanan shekarar ta bayar da magani ga ƙananan yara 52,725 masu fama da ƙarancin abinci mai gina jiki a arewacin Najeriya.

Shugaban MSF, Dr Christos Christou, ya shaida wa manema labarai a Abuja a ƙarshen mako cewa adadin yara masu fama da ƙarancin abinci mai gina jikin ya ninka a arewacin Najeriya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Talla

Ya ce daga watan Janairu zuwa Agusta, MSF ta tattara alkaluma da ke cewa an samu ƙarin ƙananan yara da ake kwantarwa asibiti saboda da kashi 51 cikin 100.

APC ta tsayar da Aliyu Harazimi Rano takarar shugaban karamar hukumar Rano

”Ana cikin haka kuma sauran cutuka masu kama ƙananan yara sun samu damar shiga jikin yara da dama a Najeriya.,” in ji shi.

Talla

Dr Christou ya ƙara da cewa sun yi maganin sauran cutuka ga ƙananan yara 12,500 bayan waɗanda ke fama da matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki, lamarin da ke nuna cewa yawansu ya ruɓanya wanda aka samu a bara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...