Zanga-zanga: Sarki Sanusi ya yi Allah wadai da tashe-tashen hankula, da sace-sace a Kano

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Sarkin Kano na 16, Malam Mohammadu Sanusi II, a ranar Juma’a, ya bayyana matukar bakin cikinsa kan ta’addancin da ya faru a Kano a yayin zanga-zangar da aka yi a fadin kasa.

Da yake magana da manema labarai a fadarsa da ke Kano a ranar Juma’a Sanusi ya bayyana rasa rayuka da dukiyoyin da aka yi a matsayin abin takaici .

Sarkin ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu tare da yin kira ga iyaye da su sanya ido sosai a kan ‘ya’yansu don gudun kada a yi amfani da su wajen ta da tsarzoma.

Talla
Talla

Ya kuma bayyana barnar da aka yi a ofishin NCC, inda aka barnata Kaddarori na miliyoyin naira a matsayin koma baya ga jihar Kano.

Sanusi ya jaddada cewa ba masu kishin kano ba ne wadanda suke daukar nauyi ana yin tashe-tashen hankula a jihar .

Atiku ya jinjinawa masu zanga-zanga, ya bukaci Tinubu ya saurari koken jama’a

Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su tona asirin masu tada fitina, sannan ya shawarci jama’a da su yi addu’ar samun zaman lafiya, da ci gaba a jihar.

Sarkin ya kuma jajanta wa wadanda suka yi hasarar dukiyoyinsu a yayin zanga-zangar .

Zanga-zanga:APCn Kano ta mayar da zazzafan martani ga kalaman gwamna Abba Kabir

Ya kuma bukaci jama’a da su kai rahoton duk wani ko gungun mutanen da ke yunkurin sayar da irin kayayyakin da suka sato ga ofishin yan sanda mafi kusa domin daukar mataki cikin gaggawa.

Ya kuma jaddada cewa ta yin hakan ne za a fallasa wadanda ke da hannu wajen sata da barna tare da gurfanar da su a gaban kuliya.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa da fari dai an fara zanga-zangar adawa da tsadar rayuwar cikin lumana, daga baya ta rikide zuwa tashin hankali a rana ta farko a Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...