Zanga-zanga: Kwamitin zaman lafiya ya yi Allah-wadai da lalata kaddarori a Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Kwamitin zaman lafiya na jihar Kano ya yi Allah-wadai da afkuwar munanan al’amura yayin gudanar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a jihar.

Kwamitin ya bayyana hakan ne ta cikin wani saƙon murya da shugaban sakatariyar (Amb. Ibrahim Waiya) ya aikowa kadaura24, ta hannun mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai Bashir A Bashir.

Talla
Talla

Kwamitin zaman lafiyar ya bayyana takaicinsa bisa yadda matasa suka ba da ƙofa ga wasu suka rika amfani da su wajen lalata kadarorin gwamnati, da na ƴan kasuwanni da sunan siyasa.

Amb. Waiya ya cigaba da cewa tun farko shugabannin zanga-zangar suna da laifi duba da yadda aka bayyana musu abun da ka iya faruwa idan suka ce sai sun gabatar da wannan zanga-zanga amma su ka yi burus da wannan kiraye-kiraye su ka fita sai gashi abunda suke hange ya afku.

Atiku ya jinjinawa masu zanga-zanga, ya bukaci Tinubu ya saurari koken jama’a

Waiya ya kuma nuna takaicin sa bisa kwashe kayan ofishin hukumar Sadarwa ta ƙasa dake hanyar zuwa gidan gwamnati, inda ya ce ba iya kanawa ne su ka yi asara ba har da jihohin arewa maso gabas, domin shi ne guri ɗaya tilo da Najeriya ta samar domin koyar da al’ummar arewa harkokin sadarwa.

A ƙarshe Waiya ya ja hankalin masu haɗa wannan husuma, inda ya tunatar dasu gobe ƙiyama domin rai zata girbi duk abinda ta shuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...