Gwamnan Kano ya nada sabbin Sarakuna 3 masu daraja ta biyu

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin sabbin sarakunan da zasu jagoranci masarautun Rano, Gaya da Kuma karaye a matsayin sarakuna masu daraja ta biyu.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Talla

Sarakunan da aka nada sun hadar da Alhaji Muhammad Mahraz Karaye a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin nadin nasa shi ne hakimin karamar hukumar Rogo.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya sanya hannu a sabuwar dokar karin masarautu

Sai Alhaji Muhammad Isa Umar a matsayin Sarkin Rano wanda kafin nadin nasa shi ne hakimin karamar hukumar Bunkure.

Sai kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya a matsayin Sarkin Gaya wanda a baya shi ne tsohon Sarkin masarautar Gaya wadda aka rushe.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hori sabbin sarakunan masu daraja ta biyu da su zamo masu hada kan al’umarsu da tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa al’adu a masarautunsu daban daban.

Sanarwar tace nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...