ASUU ta yi fatali da nada Gawuna da wasu a matsayin shugabannin gudanarwar da jami’o’in a Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU reshen jami’ar Bayero ta Kano, ta yi watsi da nadin da aka yiwa Dakta Nasiru Gawuna a matsayin shugaban majalisar gudanarwar jami’ar.

Kadaura24 ta rawaito shugaban kungiyar, Farfesa Ibrahim Tajo Suraj ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a Kano.

Ya ce tsarin da aka bi har aka nada ‘yan siyasa a majalisun gudanarwar manyan makarantun ilimi na kasa ya saba wa dokokin da aka samar domin irin wannan nade-naden.

Gwamnan Kano ya zargi gwamnatin Ganduje da ɗaukar nauyin harkar daba a jihar

“Dole ne mu bayyana rashin jin dadinmu akan matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na nada manyan ‘yan siyasa a majalisar gudanarwar jami’o’i wanda hakan bai daidai ba”.

Siraj ya jaddada cewa “Sharuɗɗan irin waɗannan nade-naden a bayyane suke, domin suu fifita nada ƙwararrun malamai a Majalisar gudanarwar”.

Rikicin Sarautar Kano: Yan Sanda Sun Dauki Bangare – Gwamnan Kano

Shugaban ya kara da cewa korar tsohuwar majalisar da kundin tsarin mulki ya ba ta wa’adin shekaru 4, bayan sun yi shekara daya a ofis

Don haka ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta mayar da Sanata Udo Udoma shugabancin majalisar gudanarwar kasar domin kammala wa’adinsu domin tabbatar da doka da oda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya...

Aiyuka 5 da Gwamnan Kano ya yi alkawarin yi, bayan dakatar da rusau a Rimin Zakara

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci garin Rimin Zakara...

Shugaban K/H Garun Mallam zai Raba Audugar Mata 500 ga Makarantun Sakandiren Matan yankin

Daga Safiyanu Dantala Jobawa Shugaban karamar hukumar garun mallam Aminu...

Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...