Ya kamata Gwamnatin Kano ta Mutunta Umarnin Kotu – Dr. JY

Date:

Daga Rahama Usman

 

Tsohon kwamishinan harkokin noma na jihar kano Dr. Yusuf Jibril JY ya bukaci gwamnatin jihar da ta bi umarnin kotun tarayya na tabbatar da dawo da Sarakunan Rano Gaya Bichi da Karaye.

” Muna da kyakykyawan yakinin gwamnatin za ta mutunta umarnin kotu saboda ta amfani hukuncin kotu don haka ita yafi dacewa ta mutunta umarnin don kiyaye doka da Oda”.

Yanzu-yanzu: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Sarautar Kano

Dr. Yusuf Jibril JY ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da jaridar kadaura24, jim kadan bayan hukuncin kotu.

Ya ce mutunta umarnin kotun zai kara fito da kimar gwamnatin, amma rashin bin umarnin kuma zai zubar da kimar gwamnatin a idon al’ummar jihar kano da kasa baki daya .

Hadimin gwamnatin Kano ya yiwa Kawu Sumaila, Hanga da yan majalisu 17 wankin Babban Bargo kan rikicin Sarauta Kano

Dr. JY ya bukaci al’ummar jihar Kano da su gudanar da murnar dawo da Sarakunan su cikin kwanciyar hankali da lumana, ba tare da karya doka ba.

” Ina amfani da wannan dama wajen taya mai martaba Sarki Rano Alhaji Dr. Kabir Muhammad Inuwa, bisa dawo da shi kan karagarsa ta Sarautar Rano wadda aka ba cire shi ba bisa ka’ida ba”. A cewar Dr. JY

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiya Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...