Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Shugaban Nigeria Bola Tinubu yayi alkawarin bada lambar yabo ga yan wasan Kwallon kafa na super eagles da suka buga wasa a AFCON 2024.
Hakan na cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan shafukan sada zumunta Olusegun Dada a shafin sa na X a ranar Talata.
Wata Kungiya Ta ce Zata Maka Gwamnan Kano a Kotu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa dukkan membobin kungiyar Kwallon kafa ya Najeriya lambar yabo ta member na Order of Niger (MON),” kamar yadda tweet din ya karanta.
Yan Hisbah a Kano Sun Kama Tauraruwar TIKTOK
Ya kara da cewa, Tinubu ya yabawa ‘yan wasan da daukacin yarin Nigeria da suka halarci wasan cin kofin zakaran Kasashen Africa, bisa jajircewar da suka yi da kuma daga darajar al’ummar kasar a gasar AFCON da aka kammala kwanan nan,
” Duk da cewa ba mu ji dadin rashin nasarar da da bamu samu ba, amma Super Eagles sun nuna bajintar wasanni kuma sun yi iya bakin kokarin su”.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a ranar Lahadi Kasar Ivory Coast ta Lallasa Nigeria da ci 2 da 1 a wasan karshen da Cin kofin zakaran Kasashen Africa wato AFCON 2024.