Wata Kungiya Ta ce Zata Maka Gwamnan Kano a Kotu

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Kungiyar Hadakar Jam’iyyun Siyasa (IPAC) a Jihar Kano, ta yi barazanar maka gwamnatin jihar a kotu kan yunkurin nada kantomomi a Kananan Hukumomi 44 a jihar.

Wannan na zuwa ne, biyo bayan cikar wa’adin mulkin shugabannin kananan hukumomi a jihar.

IPAC ta bai wa gwamnatin wa’adin kwanaki bakwai don janye kudurinta na nada kantomomi a kan kujerun kananan hukumomin ko kuma ta maka ta a gaban kuliya.

Yan Hisbah a Kano Sun Kama Tauraruwar TIKTOK

Kungiyar ta yi zargin Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fara yunkurin nada ma’aikatan da ya kai kananan hukumomin a kwanakin baya don zama kantomomi.

 

Kungiyar ta ce Abba ya nemi shugabannin kananan hukumomin jihar da su mika ragamar mulki ga shugabannin mulki na kananan hukumominsu.

Sarkin Kano ya Baiwa Matar Tinubu Sako Zuwa ga Shugaban Kasa

Wakilin kungiyar a bangaren sharia, Barista Salisu Salisu Umar, ya ce yunkurin wani mataki ne na take hakkin al’umma.

Jam’iyyun siyasa 12 da suka hada da ADC da Accord da YPP da PRP da APGA da AAC da APC da Labour da APM da ADP suka sanya hannu kan hana gwamnan nada kantomomi.

A cewarsa “Kananan hukumomin su ne to turke na uku a Gwamnatin Najeriya. Sashe na 7 (1) na Kundin Tsarin Mulkin Kasa na shekarar 1999, ya hana nada kantomomi sai dai batun zabe.”

A cewar Barista Salisu, “Wannan abu da Gwamnatin Jihar Kano ke kokarin yi keta alfarmar dimokuradiyya ne wanda kuma ba za mu nade hannu muna kallon hakan ya faru ba.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...