Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Kano ta Soke lasisin duk Makarantu Masu Zaman Kansu a jihar

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta soke lasisin dukkanin wasu makarantu masu zaman kansu da ke aiki a jihar.

 

Majiyar Kadaura24 ta Daily Telescope ta rawaito cewa an dauki matakin ne a ranar Asabar yayin ganawa da mammalla makarantu masu zaman kansu da gwamnatin jihar kano.

Talla

Mai baiwa gwamna shawara na musamman kan makarantu masu zaman kansu da na sa kai, Alhaji Baba Abubakar Umar ya bayyana cewa ana bukatar dukkan makarantu masu zaman kansu da su je domin sabunta rijistar su cikin gaggawa, saboda gwamnati zata fara bayar da sabbin satifiket ga makarantun.

Sojojin Kasar Burkina Faso Sun Dakatar Da Gidan Rediyo Sakamakon Sukar Juyin Mulkin Nijar

Baba Umar ya bayyana cewa matakin ya jaddada kudirin gwamnati na ganin cewa makarantu masu zaman kansu sun bi ka’idojin da aka gindaya na gudanar da makarantu masu zaman kansu a jihar yadda ya dace .

“Muna tunatar da masu makarantu masu zaman kansu alhakin da ya rataya a wuyansu na biyan harajin kashi 10 ga gwamnati. Wannan alƙawarin kuɗi koyaushe yana haɓaka ci gaba a fannin ilimi da tattalin arziki.” in ji shi.

 

Mashawarcin na musamman ya tabbatar wa duk masu ruwa da tsaki cewa zai tabbatar da Adalci wajen kula da harkokin makarantu masu zaman kansu.

Ba Zamu Bari Yunkurin Juyin Mulki yayi Nasara a Nigeria ba – Rundunar Soji

Mai ba da shawara na musamman ya kuma tabbatar wa iyayen dalibai cewa zasu cigaba da basu fifikon wajen kiyaye muradun su da na ‘ya’yansu.

Da yake mayar da martani, shugaban kungiyar masu makarantu masu zaman kansu reshen jihar Kano, Alhaji Muhammad Malam Adamu, ya yaba da matakin da gwamnati ta dauka, yana mai kallon matakin a matsayin abin yabawa a fannin ilimi .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...