Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ‘ya’yansa biyu da wasu mutum shida kotu bisa zargin yin almundahanar kudi naira biliyan 4.49.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa an shigar da karar ne a babbar kotun jihar Kano a ranar 13 ga Oktoba, 2025, inda gwamnati ke neman a maido da kashi 20 cikin 100 na kudaden da aka zuba a Dala Inland Dry Port Limited, da kuma dawo da kudin da ake zargin an karkatar.

InShot 20250309 102512486
Talla

Wadanda ake tuhuma sun hada da Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ‘ya’yansa Umar da Muhammad, tsohon mai ba shi shawara Abubakar Sahabo Bawuro, tsohon sakataren hukumar Nigerian Shippers Council Hassan Bello, lauya Adamu Aliyu Sanda, da kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

A cewar takardar tuhumar, ana zargin wadanda ake tuhumar da laifuka goma da suka hada da hada baki wajen karkatar da kudaden al’umma, cin amana da kuma sabawa doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...