Ba Zamu Bari Yunkurin Juyin Mulki yayi Nasara a Nigeria ba – Rundunar Soji

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Rundunar Sojin a Nijeriya ta ce akwai wasu marasa kishin ƙasa da ke zuga su, su kifar da gwamnatin dimokuraɗiyya, wacce shugaba Bola Ahmed Tinubu ke jagoranta.

 

Daraktan yaɗa labarai na rundunar, Birgediya-Janar Tukur Gusau ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aike wa Daily Trust da sanyin safiyar yau Asabar, inda ya bayyana yunƙurin a matsayin rashin kishin ƙasa da kuma zalunci.

Talla

Sai dai kuma rundunar sojin ta ce wannan yunƙurin ba zai samu nasara ba duba da cewa sojoji na jin daɗin mulkin dimokuraɗiyya kuma za su yi duk me yiwuwa domin kare dimokradiyya a ƙasar.

Iftila’i Babban Masallacin Zazzau ya rufta ana sallah

A cewar Janar Gusau, sojoji za su ci gaba da aikin su da kundin tsarin mulki ya kallafa musu maimakon ɓata lokacinsu wajen yunƙurin kifar da gwamnatin dimokuraɗiyya wacce aka sha jan aiki wajen kafa ta, inda ya kara da cewa sojin Nijeriya ba za su kau da hankalin su wajen kokarin kare mutunci, martaba da zaman lafiyar ƙasar ba.

Wannan batu ya zo ne dai-dai lokacin da wasu ke kira da sojoji su karɓi ragamar mulki, inda a ganin su, dimokradiyya ta gaza.

A halin yanzu haka sojoji sun kifar da gwamnatin Mohamed Bazoum a Nijer, inda ECOWAS ke fafutukar ganin an maido da gwamnatin dimokuraɗiyya a ƙasar dake makwabtaka da Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...