NAHCON ta ayyana ranar da za’a fara dawo da Alhazan Nigeria gida

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Hukumar kula da aikin hajji ta Nigeria NAHCON, ta bayyana cewa zata fara aikin jigilar mayar da alhazan kasar gida daga kasar Saudiyya a ranar talata 04vga watan yuli 2023.

Shugaban dake kula da sashin harkokin jiragen sama na hukumar, Alhaji Goni Sanda ne ya bayyana hakan, yayin wani taro da hukumar ta gudanar a garin Makka na kasar Saudiyya.

Talla

Ya ce tsarin wanda ya fara zuwa shi zai fara dawo wa, shi za’a yi amfani da shi wajen jigilar alhazan zuwa Najeriya.

Sallah: Gwamnan Kano ya nemi afuwar Sarkin Gaya kan abun da ya faru a gidan gwamnati yau

Gwani Sanda ya kara da cewa, mahukuntan Saudiyya sun yi tsarin cewa a cikin makonni biyun farko jiragen ba za su yi aiki sosai ba, saboda yawan zirga-zirgar jiragen sama dake kwashe alhazan su zuwa kasashe daban-daban, sannan kuma da kasancewar kusan dukkan jirage za su tashi ne daga filin jirgin sama guda daya, na Sarki Abdulaziz, dake Jeddah.

Ya bayyana cewa a cikin makonni biyun farko na fara jigilar maniyyatan, jirgin kamfanin Flynas zai yi amfani da jiragen guda hudu ne kawai daga cikin su shida, domin gudanar da aikin, inda ya kara da cewa sauran biyun ana bincike akan su domin basu kulawar da ta dace .

Har ila yau, kwamishinan ayyuka na NAHCON, Alhaji Abdullahi Hardawa, ya ce hukumar ta kudiri aniyar tabbatar da cewa maniyyatan sun yi cikkakiyar biyayya ga manufofinta na jigilar kaya yayin mayar da su Najeriya.

Ya yi tir da halin wasu alhazai musamman mata da ke zuwa filin jirgin sama dauke da jakunkuna da yawa duk da sunan kayan hannu, yana mai gargadin cewa a wannan karon ba za a amince da lamarin ba.

Don haka ya yi kira ga jami’an hukumomin alhazai na jihohi da su sanar da alhazansu manufofi da tsare-tsaren don gujewa duk wata matsala da bata lokaci a filin jirgin.

“Kamfanonin jiragen sun koka matuka game da wannan hali na wasu alhazai, wanda ke jefa rayukan sauran fasinjojin da ke cikin jirgin cikin hadari. Wannan karon ba mu bari ba kamar yadda aka saba ba.

“Kuma saboda tsoron rasa wasu kayayyaki masu mahimmanci a filin jirgin sama, ya kamata mahajjata su bi ka’idojin jigilar kaya a jakunkuna da aka basu masu daukar kayan da basu wuce nauyin 32kg ba.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...