Ayyukan ta’addanci: akwai yiwuwar samun Karancin abinchi a Arewacin Nigeria – Bafarawa

Date:

Rikicin ƙarancin abinci na shirin kunno kai a Arewa sakamakon ayyukan ƴan bindiga – Bafaraw

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, kuma mamba a kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya nuna damuwarsa kan ayyukan ƴan bindiga a yankin Arewa-maso-Yamma da kuma Arewa-maso-Gabas, inda ya bayyana fargabar cewa hakan ka iya haifar da matsalar karancin abinci.

 

Bafarawa ya kuma yi gargadin cewa idan ba a dauki tsauraran matakai na dakile tashe-tashen hankula ba, Arewa za ta fuskanci koma bayan ilimi mai tsanani.

Talla

Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne a wata hira da jaridar PUNCH a jiya Lahadi.

Sallah: Gwamnan Kano ya nemi afuwar Sarkin Gaya kan abun da ya faru a gidan gwamnati yau

A cewarsa, ya kamata sabuwar gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta dauki batun samar da abinci a matsayin daya daga cikin abubuwan da ta sa gaba.

 

Bafarawa ya ce, “Maimakon maganar naɗin ministoci, tallafin mai da kuma tattalin arziki, kamata ya yi gwamnati ta yi la’akari da batun samar da abinci domin a halin da muke ciki, nan da watanni uku masu zuwa, tabbas za mu fuskanci matsaloli a Najeriya, musamman a Arewa-maso-Yamma.

NAHCON ta ayyana ranar da za’a fara dawo da Alhazan Nigeria gida

“’Ƴan bindiga sun ki barin manoma su yi noma. Wannan lamari dai ya na da matukar hadari, ba wai kawai yan bindigar na kashe mutane ba, har ma da karancin abinci zai yi tsanani nan da wasu watanni masu zuwa, musamman a yankin Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas. Don haka mu na son gwamnati ta farka ta yi wani abu a kai,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...