Cibiyoyin dake kula da waɗanda zafin rana ya illata a wuraren ibada masu tsarki na ƙasar Saudiyya na ci gaba da samun hauhawar mutanen da ake kwantarwa saboda jigata.
Ana alaƙanta lamarin da gazawar mahajjata wajen bin ƙa’idojin kare kai daga tsananin zafin rana da ake a kasar Saudiyya.

Ma’aikatar Lafiya ta Saudiyya ta faɗakar da mahajjata game da hatsarin tsananin zafin rana, inda ta buƙace su da su riƙa sanya ɓaƙin tabarau da kuma shan ruwa sosai, sannan su guje wa zirga-zirgar da ba ta wajaba ba.
Ganduje ya Magantu kan dakatar da albashin ma’aikata dubu 10 da gwamnatin Kano ta yi
Haka nan ma’aikatar ta buƙaci maniyyatan da su guje wa tsayuwa na tsawon lokaci.
BBC Hausa ta rawaito Ma’aikatar ta ce a halin yanzu waɗanda tsananin zafin ranar ya kwantar sun kai 6,700 tun bayan fara aikin hajjin bana.
A jiya an samu irin wannan matsala mafi yawa, inda zafin ya illata mutum 2,200, cikinsu har da mutum 261 waɗanda suka shiga mummunan yanayi.