Akwai yiwuwar Man fetur ya sake tashin gwauron zabi a Nigeria – IPMAN

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Ƙungiyar dillalan man fetur masu zaman kansu a Najeriya ta ce akwai yiwuwar nan da lokaci kaΙ—an farashin man fetur zai zarce naira 600 a kan kowace lita.

 

IPMAN ta ce hakan zai faru ne sanadiyyar rashin tabbas kan samuwar dala ga Ζ΄an kasuwa masu shigo da tataccen man fetur daga Ζ™asashen waje.

Ganduje ya Magantu kan dakatar da albashin ma’aikata dubu 10 da gwamnatin Kano ta yi

Bayanai sun nuna cewa da zarar ‘yan kasuwa masu zaman kansu suka fara shigo da man fetur a wata mai kamawa, farashin litar mai zai haura sama a faΙ—in Ζ™asar.

Tallah

A lokacin da yake tabbatar wa BBC da wannan batu, shugaban Ζ™ungiyar dillalan man fetur Ι—in a yankin Arewacin Najeriya, Bashir Dan-Mallam ya ce dole ne sai gwamnati ta Ι—auki matakan da suka dace domin hana faruwar hakan.

Dan-Mallam ya ce samuwar dalar a wadace ga Ζ΄an kasuwa za ta hana hauhawar farashin na litar mai.

A yanzu dai kamfanin man fetur na Ζ™asar NNPC ya ce zai riΖ™a shiga da kashi 30% na man fetur Ι—in da Ζ™asar ke buΖ™ata, yayin da Ζ΄an kasuwa za su shigar da sauran.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023 ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur, wani lamari da ya haifar da tashin farashin litar man fetur a faΙ—in Ζ™asar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related